Hukuncin Iyaye Masu Hana ‘Ya’yansu Yin Azumi

| |times read : 293
  • Post on Facebook
  • Share on WhatsApp
  • Share on Telegram
  • Twitter
  • Tumblr
  • Share on Pinterest
  • Share on Instagram
  • pdf
  • Print version
  • save

Hukuncin Iyaye Masu Hana ‘Ya’yansu Yin Azumi

Mene ne hukuncin iyaye maza da mata wadanda suke hana ‘ya’yansu wadanda ba su jima da balaga ba yin azumi da hujjar cewa har yanzu su yara ne kanana kuma wai ba za su iya yin azumin ba? Kuma mene ne ya hau kan ‘ya’yan game da wannan?

 

Da Sunansa Madaukaki

Wannan aikin nasu bai halasta ba kuma ya sabawa tsantseni, domin lallai wannan yana daga cikin abubuwa masu sauki a addini sannan wajibi ne a kansu su dinga karfafa ‘ya’yansu maimakon raunana su, su dinga koyar da su yin azumin tun kafin su balaga ta yadda lokacin da suka balaga zai zama mai sauki a gare su. Amma ga su ‘ya’yan to wajibi ne a kansu su dauki azumi, domin babu biyayya ga abin halitta a cikin sabawa mahalicci, kuma idan aka tilasta masu cin abinci to dole ne su yi ramuwa daga baya. Amma idan tsoron da ake ji na yin azumin tabbatacce ne, to wannan zai iya zama dalilin da za a ajiye azumi, amma ba wajibi ba ne a ci gaba da wannan aikin koda akwai cutuwar ba.