Fatawa Dangane Da Zagin Ababen Girmamawa Na Addini Na ‘Yan Uwa Ahlussunah.

| |times read : 382
  • Post on Facebook
  • Share on WhatsApp
  • Share on Telegram
  • Twitter
  • Tumblr
  • Share on Pinterest
  • Share on Instagram
  • pdf
  • Print version
  • save

Fatawa Dangane Da Zagin Ababen Girmamawa Na Addini Na ‘Yan Uwa Ahlussunah.

Da Sunansa Madaukaki

Samahatul Marja’in Addini Ayatullah Al-Uzma Shaikh Muhammad Yakubi (Allah Ya Tsawaita Kwanakinku)

Ya shugabanmu mai girma, a ranar shahadar Imam Muhammad Jawad (as) an samu taron wasu matasa da suka fito suna zagin abubuwan girmamawa na addina na ‘yan uwa ahlusunnah.

To mene ne ra’ayinku dangane da wannan kuma wace nasiha ce za ku yi wa al’ummar musulmai game da hakan? 

Da Sunansa Madaukaki

Assalamu Alaikum Warahmatullah wa Barakatuhu

Wannan abin ai wauta ce tsagwaronta da aikin jahilci, ba shi da wata alaka da koyarwar Ahlul Bait (as), kuma lallai ba na raba daya biyu cewa akwai wani boyayyen hannu wanda yake kara ruruta wutar fitinar nan da kambamata daga bangarori nan guda biyu, don haka mu al’ummar Musulmi tare da dukkan sabanin fahimtarmu muna da matukar bukatar taka-tsantsan da sanya ido a kan wannan bakar fitina, kuma a baya ma na tsawatar da mu a kanta a cikin zance na mai taken (Kaidin shaidan don gurbata yankunanmu), kuma mun gargadi jama’a a kan haka.

 

 

 Muhammad Al- Yakubi  

7/Zulhijja/1434 AH.