wasa (clash of clans)
Da Sunansa Madaukaki
Marji’in Addini Samahatul Shaikh Muhammad Yakubi (Da fatan Allah ya yawaita albarkarsa a gare ka).
A kwanukan baya-bayan nan a cikin wannan zamanin namu akwai wani wasan da ya yadu wanda ake yinsa a cikin wayar hannu da kwanfuta wanda aka lakabawa suna da (clash of clans). Wannan wasan yana daukar lokuta masu yawa na samari, sannan wasu suna sayar da wasan har su amshi kudi daga hannun wasunsu. Yadda wannan wasa yake kuwa shi ne wani wasa ne da ya kumshi girka rundunar sojoji da gina masu gari tare da katange garin, sannan sai a dinga kai hari ga makiya domin a tara maki, to duk lokacin da makin wannan gari ya yi yawa to daraja da tsadar garin za su yi sama, kamar kuma yadda dan wasan zai dinga rugurguza duk wani babban mutumin da aka kaddara samuwarsa a cikin wadancan makiya din. To kamar dai yadda ku ka sani ya samahatul shaikh cewa bahasosin ilimi na baya-bayan nan sun tabbatar da cewa wasu daga cikin wasannin kwamfuta (na zamani) suna kara rura wutar kiyayya a tsakankanin yara da matasa, kari a kan irin lokutan da irin wadannan wasannin na kwamfuta suke cinyewa a cikin gidaje ne ko a gidajen kallon wasanni da shagunan masu sayar da neskafi, kuma wannan wasan kai tsaye yana jan hankalun yara da matasa ta hanyar canja masu nauo’in dabi’unsu a rayuwa. Shin samahatul shaikh ko wannan wasan yana halasta a yi shi, kuma ko yana halasta a shiga cikin gidajen da ake yinsa.
Muna jiran amsarku, mun gode.
Da Sunansa Madaukaki
Assalamu Alaikum Wa Rahmatullah Wa Barakatuhu
Mun yi bincike a kan wannan wasa da yadda ake yinsa da wadanda ake yin wasan da su, sai muka samu cewa akwai wadansu abubuwa wadanda suke tilasta yin hani ga aiwatar da shi, kuma muna da maganganu da yawa da aka yada su tun bayan faduwar gwamnatin Saddam a shekarar 2003 a yayin da muka fayyace hadurran irin wadannan wasannin ga hankulan yara da tarbiyyar jama’a, aklak dinsu, addininsu da tattalin arzikinsu, kuma wadannan kadai sun isa su sa a hana yin wadannan wasanni.
A saboda haka muna yin nasiha ga waliyyai da su sanya ido a kan matasansu domin katange su daga wannan hadarin kuma su kula sosai a kan gabaki dayan kai-komonsu, kamar yadda muke yin kira ga shuwagabannin kananan hukumomi da na jahohi a kan su kafa doka da kuma gudanar da ita a kan masu gidajen kallo da shagunan shan neskafi, domin kada ya zama an barsu har su fi muhimmatar da tara dukiya a kan gyara tarbiyyar yaranmu da kasarmu, a wajen Allah muke neman taimako.
Muhammad Yakubi
8 ga Rabi’ul Sani 1437 AH.